Dakarun Tafkin Chadi Sun Yi Wa ‘Yan Boko Haram Rugu-rugu

—VOA Hausa

Rundunar dakarun Tafkin Chadi sun yi wa mayakan Boko Haram dirar mikiya inda suka hallaka da dama daga cikin su ta bangaren Najeriya, yayin da su kuma aka yi masu kofar rago daga Marwan a kasar Kamaru.

Kwamandan runduna ta daya ta dakarun kasasahen yankin Tafkin Chadi, Brigadier General Bouba Dobekreo ya yi wa Muryar Amurka bayani dangane da hare-haren da suka kai a kasashen Najeriya da Kamaru, al’amarin da yayi sanadiyyar rugurguza baki dayan sansanonin mayakan Boko Haram na wannan shiyya.

Brigadier General Bouba Dobekreo ya kara da cewa mayakan sun yi kokarin arcewa yayin da suka yi ta tsallakawa kan iyakar Najeriya sannan sojojin sun yi nasarar kwato wasu daga cikin kayayyakin yakin ‘yan ta’addan.

Babban kwamandan runduna ta 7 ta sojojin Najeriya, Brigadier General Abdul Khalifa Ibrahim ya kara zaburar da dakarun bataliyar da ke karkashin rundunarsa a shirye-shiryen da suke yi don tunkarar mayakan na Boko Haram a shiyyar iyakar Najeriya da Kamaru.

Brigadier General Abdul Khalifa Ibrahim ya cewa sojojinsu suna nan suna aiki tun daga wajen iyakar Najeriya har zuwa wuraren dajin Sambisa, kuma suna nan suna sintiri, sannan sun shirya wannan farmakin ne saboda samun labarin sirrin cewa shugabannin ‘yan ta’addan suna bin hanyar. An hallaka 6 daga cikin shugabannin wasu da dama kuma sun jikkata a farmakin.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...