
Dakarun sojan Najeriya sun kashe akalla yan ta’adda 30 a wasu jerin hare-haren ta sama da su ka kai musu a yankin tafkin Chadi a jihar Borno.
A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya bayyana cewa gamsassun bayanan sirri da aka tattara ta hanyar amfani da jiragen sama da wasu naurori ya nuna cewa yan ta’addar suna tattaruwa a tsibirin Kaniram.
A shawagin tattara bayanai da jirgin leken asirin sojan su ka yi sun nuna jiragen ruwa kusan 31 da kuma mayakan kungiyar yan ta’adda ta ISWAP.
Harin farko da jiragen yakin suka kai ya ya lalata jiragen ruwan.
Bom na biyu da aka harba ya fada kan yan ta’addar su kusan 8 a dai-dai lokacin da su ke kokarin buya.
Bom na uku ya fada kan gungun wasu yan ta’addar su sama da 15 a yayin da su ka buya a kasan wata bishiya.
A cewar Zagazola binciken da aka yi byan tattara bayanai kan tasirin harin ya nuna irin mummunan barnar da hare-haren su ka yi wa yan ta’addar.

