Buhari Zai Dauki Sabbin ‘Yan sanda Dubu 10 A Aiki

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya ba da umarnin a dauki sabbin ‘yan sanda dubu 10,000 a kasar.

Mai taimakawa Buhari a fannin yada labarai ta kafafen zamani Bashir Ahmad ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa.

“Shugaba Muhammadu Buhari ya ba da umarnin a dauki ‘yan sanda 10,000 a matsayin jami’an ‘yan sanda a jihohi 36 da babban birnin tarayyar Abuja.” Ahmad ya ce.

An dauki wannan mataki ne, “don a tunkari kalubalen tsaro a wasu sassan kasar.”

A cewar sanarwar, an dauki mutum 10 ne a kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomi 774 da ke Najeriya, kuma tuni har an sanar da wadanda aka dauka ta hanyar emel da suka nemi aikin.

Daukan karin ‘yan sanda a aiki na zuwa ne yayin da Najeriya ke fuskantar matsalolin tsaro a sassanta.

A Arewa maso yammacin kasar na fama da ‘yan fashin daji da ke kai hare-hare da sace mutane domin neman kudin fansa.

Arewa maso gabashi kuma tana fama da matsalar Boko Haram da ISWAP, yayin da a kudu maso gabashin kasar take fama da matsalar ‘yan awaren kungiyar IPOB.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...