Buhari ya yi kira ga ‘yan fashin daji su yi saranda

Shugaban Najeriya muhammadu Buhari
Hakkin mallakar hoto
Buhari Sallau
Image caption

Buhari ya jajantawa mutanen Katsina

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jajantawa al’ummar jiharsa ta Katsina kan hasarar rayukan da aka samu sakamakon hare-haren ‘yan bindiga.

A makon da ya gabata ‘yan bindiga suka kashe mutane da dama a Katsina cikinsu har da hakimin Yantumaki Alhaji Atiku Maidabino, da shugaban Jam’iyyar APC na karamar hukumar Batsari Alhaji Abdulhamid Sani Duburawa.
Sanarwar da Malam Garba Shehu ya fitar mai taimakawa shugaban kan harakokin watsa labarai a ranar Asabar ta ce, shugaban ya gana da gwamna Aminu Bello Masari a ranar Alhamis kan matsalar tsaro da ta addabi yankin arewa maso yammaci.
Kuma shugaban ya kara bai wa gwamnan da al’ummar jihar Katsina tabbaci kan sabon kokarin da ake na inganta tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar da sauran sassan kasar.
Sanarwar ta ce yayin ganawar, Buhari ya yi kira ga ‘yan fashin daji su fito su yi saranda su mika makamansu ko kuma su kuka da kansu.
“Ba za a yafe wa ‘yan fashin da suka kashe wadanda ba su ji ba su gani ba a jihar da duk fadin kasar nan ba,” in ji shi.

  • Aisha Buhari: ‘Matsalar fyade na tayar mini da hankali’
  • Mulkin Buhari: Shin kwalliya ta biya kudin sabulu?

Shugaban ya kuma ce za a kara kaddamar da farmaki kan masu fashin daji a jihohin Zamfara da Sokoto da Neja da Katsina da Kaduna.
A makon da ya gabata ne gwamnan Katsina Aminu Bello Masari ya shaida wa BBC cewa ba zai sake yin sulhu da ‘yan fashi ba saboda sun ci amanar gwamnati.
An dade jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna na fama da hare-haren ‘yan fashin daji masu satar shanu da garkuwa da mutane domin kudin fansa, kafin su tsallaka zuwa Sokoto da Neja.

More News

Za a rataye wanda ya ɗaba wa wani wuƙa har lahira

An yanke wani mutum mai suna Hamza Mohammed  hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan da ya daba wa wani mutum wuka har lahira a...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...