Shugaban kasa Muhammad ya magana da shugabannin hukumomin tsaron kasar a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Majalisar tsaron ta kunshi dukkanin shugabannin hukumomin tsaro da kuma mai bawa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro.
Taron majalisar na yau na zuwa ne dai-dai lokacin da batun tsaro ke cigaba da tabarbarewa a fadin kasa baki daya.
A baya dai anyi ta kira-kirayen da Buhari ya sauya shugabannin rundunar sojan kasar sai dai shugaban ya ce ya gamsu da salon yadda suke gudanar da aikinsu.