Majalisar tsaron ta kunshi dukkanin shugabannin hukumomin tsaro da kuma mai bawa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro.
Taron majalisar na yau na zuwa ne dai-dai lokacin da batun tsaro ke cigaba da tabarbarewa a fadin kasa baki daya.
A baya dai anyi ta kira-kirayen da Buhari ya sauya shugabannin rundunar sojan kasar sai dai shugaban ya ce ya gamsu da salon yadda suke gudanar da aikinsu.





