Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari garin Geidam da ke Jihar Yobe, inda suka ƙone motoci huɗu ciki har da wata babbar mota ɗauke da kayayyakin ‘yan kasuwa na miliyoyin Naira.
Rahotanni sun ce harin ya faru ne da safiyar Juma’a lokacin da yawancin mazauna garin ke barci.
Maharan sun fara kai hari sakatariyar Ƙaramar Hukumar Geidam, inda suka ƙone motar Toyota Hilux da wata motar bas mallakin ƙaramar hukumar.
Daga nan suka ƙona wata babbar mota da ke ɗauke da kayayyakin ‘yan kasuwa da suka zo kasuwar mako-mako ta Geidam, tare da wata mota da aka ajiye a kasuwar.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa maharan sun shiga garin ne a ƙafa bayan sun bar baburansu a wajen gari.
Rahotanni sun nuna cewa ba a samu asarar rai ko jikkata ba sakamakon harin.
Mazauna yankin sun yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara tsaurara matakan tsaro domin hana sake aukuwar irin waɗannan hare-hare.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da faruwar harin.
Boko Haram Sun Ƙone Motoci Guda Huɗu

