BBC ta bude gasar rubutu a harshen Pidgin | BBC Hausa

Wani likita yana rubutu da biro kan takarda

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Za a lashe kyautar sama da naira 180,000

Sashen Turancin broka wato BBC Pidgin ya kaddamar da gasar rubutun zube da harshen Pidgin a ranar Alhamis 1 ga watan Agustan 2019.

Gasar a bude take ga dukkanin daliban manyan makarantun gaba da sakandare a nahiyar Afirka.

Masu sha’awar shiga gasar za su rubuta makala ne mai kalmomin da ba su wuce 800 ba kan maudu’in “ko mace za ta iya jagorancin siyasa a nahiyar Afirka?” (“Is Africa ready for female political leadership?”).

Wani rukunin alkalai da suka hada da malamai da ‘yan jarida da marubuta na harshen Pidgin wadanda suka fito daga Afirka ta Yamma ne za su zabi mutum daya wanda ya yi nasara.

Wajibi ne kowacce makala ta dace da tsarin harshen Pidgin tare da bin ka’idojin rubutu.

Za a sanar da wanda ya yi nasarar ne a Legas ranar 20 ga watan Satumban 2019. Sannan za a ba shi kyautar dala $500 (kusan naira 180,000)

Za a rufe shiga gasar ne a ranar Juma’a 30 ga watan Agustan 2019.

A aiko da makala zuwa adireshin imel na bbcpidgin.essay@bbc.co.uk

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...