Boko Haram ta kashe mutum uku a jihar Adamawa

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun far wa wani ƙauye a jihar Adamawa, inda suka kashe mutum uku tare da lalata kayayyaki da dama.

Mazauna ƙauyen na Dabna da ke karamar hukumar Hong na jihar ne sun ce mayaƙan sun shigo ƙauyen ne kan babura a safiyar ranar Litinin, inda suka yi ta harba bindigogi kan mai uwa da wabi tare da sace kayan abinci da kuma magunguna.

Wani jami’in bijilanti ya ce fararen hula huÉ—u ne suka mutu a harin, inda ya Æ™ara da cewa É—aya daga cikin maharan ya rasa ransa yayin artabu da wasu jami’ansu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar Adamawa, Sulaiman Nguroje ya fitar, rundunar sun tabbatar da kai harin, inda suka yi Allah-wadai da shi.

Ya ce ya zuwa yanzu sun tura tawaga zuwa yankin domin kwantar da hankula.

A watan Yulin 2021, wasu da ake zargin ƴan ta-da-ƙayar-baya na Boko Haram suka kaddamar da hari a ƙauyen Dabna tare da kashe mutane da dama.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...