Bayan sulhu, ‘yan ta’adda sun fara sako wadanda suke rike da su a Katsina

A ci gaba da shirin sasanci da sulhu da Gwamnatin jahar Katsina take yi da masu kai hare haren ta’addanci a wasu sassa na wannan jihar, a jiya an mika mutane guda bakwai da suke tsare a hannun jami’an tsaro wadanda ba a riga aka yanke wa hukunci ba.

Ta bangaren su kuma, a shekaranjiya sun dawo da mutane biyar, (mata uku maza biyu). A jiya kuma sun sako mata guda goma da yarinya ta goye guda daya, dukkan su kuma mutanen garin Shinfida ne ta karamar hukumar Jibia.

Ana kuma jiran su sako sauran mata takwas da yara guda goma.

Ya Allah Ka dafa mana, wannan shiri yayi nasara mu sami zaman lafiya mai dorewa a wannan jiha tamu mai albarka.

More News

Rundunar Sojan Najeriya Ta Fitar Da Sunayen Sojojin Da Aka Kashe A Jihar Delta

Rundunar sojan Najeriya ta fitar da hoto da kuma sunayen sojoji 16 da aka yiwa kisan gilla a jihar Delta. Ranar Alhamis ne aka kashe...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...