Bauchi: ‘Za a rataye masu yi wa ƙananan yara fyaɗe’

Gwamnatin jihar Bauchi ta kafa wata doka da ake kira BAP wadda ta tanadi hukuncin kisa ta hanyar rataya ga duk wanda aka samu da laifin yi wa yara kanana Fyade.

Haka ma dokar ta tanadi ɗaurin rai da rai ga wanda ya yi wa babbar mace fyade da kuma ɗaurin shekaru 20 ga wadanda suka yi wa mace daya taron dangi.

Wannan dai na zuwa ne yayin da hukumomin ‘yan sanda a jihar suka ce sun samu rahotannin aikata fyade har 21 a cikin wata ɗayan da ya wuce kawai.

Ko a baya-bayan nan ma ‘yan sanda a jihar sun sanar da kama wani mutum da suke zargi da yi wa wata yarinya ‘yar shekaru uku fyade.

DSP Muhammad Ahmad Wakili, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ta Bauchi ya ce dokar tuni aka amince da ita a majalisa kuma za a wallafa ta.

A cewarsa, tsakanin watan Yuli da Agusta sun gabatar da mutum 22 da ake zargi da aikata fyade gaban ‘yan jarida.

Ya ce sun yi hakan saboda “muna son mutane su kyamaci wannan abin su gane cewa idan an yi wa mace fyaɗe mai da al’uma baya ne saboda har ta gama rayuwarta da wannan (ƙyamar da ake nuna mata).”

DSP Wakili ya ce laifin fyaɗe ba wai yarinyar da aka yi wa ya shafa ba, laifin ya shafi ƙasa ne.

“Duk wanda muka kama ya yi fyaɗe, ba za mu yi wata-wata ba, sai mun gurfanar da shi gaban kotu, kuma wannan (dokar) BAP ita za mu saka ma shi a gaban kotu.” in ji DSP Wakili.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...