Barcelona za ta sayar wa Juventus Arthur a kan £72.5m, Carvalho ya ƙulla yarjejeniya da Leicester

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Juventus ta amince ta biya euro 80m domin karbo dan wasan Barcelona mai shekara 22 dan kasar Brazil, Arthur – Amma dole ta rarrashe shi kafin ya koma can. (Sky Sports)

Dan wasan tsakiya na Portugal William Carvalho, mai shekara 28, ya cimma yarjejeniya daLeicester City, abin da ya rage kawai shi ne kungiyar ta Gasar Firimiya ta daidaita da Real Betiskan farashinsa(Marca)

Crystal Palace tana dab da da kammala sayen Nathan Ferguson bayanWest Brom ta tabbatar cewa dan kasar Ingila mai shekara 19 ya ki amsa tayin sabunta kwangilarsa. (Guardian)

Ana sa ran Arsenal za ta amince da tsawaita kwangilar dan wasan Portugal Cedric Soares wanda ta karbo aronsa dagaSouthampton kuma tana so ta sayi dan wasan mai shekara 28 gaba daya idan aka bude kasuwar musayar ‘yan kwallon kafa. (ESPN)

  • Modric ya yi wasa na 150 da Madrid ta ci a La Liga
  • Makomar Henderson, Kurzawa, Meunier, Onana

Ana sa ran dan wasan Ingila Andy Carroll, mai shekara 31, zai tsawita kwangilarsa da shekara daya a Newcastle United. (Chronicle)

West Ham, Rangers da kuma AZ Alkmaarsuna son dauko dan wasanManchester United dan kasar Ingila Dion McGhee, dan shekara 19. (Manchester Evening News)

Mamallaka West Ham suna son sayar da kungiyar bayan rahotanni sun nuna cewa wata kungiya da ke Hadaddiyar Daular Larabawa tana son sayen kungiyar. (Star)

Watakila dan wasanArsenal dan kasar Brazil Gabriel Martinelli, mai shekara 19, ba zai buga sauran wasannin kakar wasa ta bana ba sakamakon raunin da ya yi a gwiwarsa lokacin atisaye. (Mirror)

Rennes ta nemi bai wa Monaco euro 15m don dauko dan wasan Faransa Benoit Badiashile, mai shekara 19. (RMC Sport – in French)

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...