Barayin da suka sace ‘yan mata shida ‘na neman kudin fansa’

A

Hakkin mallakar hoto
Kaduna State Government

Image caption

“Maharan sun shiga makarantar ne ta bangaren da katangar makarantar ta rushe”

Mutanen da sukayi garkuwa da ‘yan matan sakandare shida da malamansu guda biyu a jihar Kaduna sun nemi a ba su kudin fansa, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito gwamna Nasir Elrufa’i ya fadi.

A daren ranar Alhamis ne dai aka sace ‘yan matan an makarantar kwana ta Engravers College da ke kusa da birnin Kakau Daji a kudancin birnin Kaduna.

“Sun nemi a ba su kudi kuma ana tattaunawa.” In ji Gwamna Nasir Elrufa’i.

Kmafanin dillancin labaran ya kuma yi magana da daya daga cikin iyayen ‘yan matan da aka sace.

“‘Yata ta kira ni da duku-dukun ranar Juma’a a waya amma ban san lambar ba.”

“Tana kuka cikin yanayin firgici.”

Za a iya cewa ba wannan ne karon farko da ake yin garkuwa da ‘yan mata ‘yan makaranta a arewacin Najeriya ba.

Sai dai masu fashin baki na ganin yanayin sace wadannan ‘yan matan ya sha banban da na baya da ‘yan kungiyar Boko Haram suka yi a Chibok da Dapchi.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]