Barayin ƙarfen digar jirgin ƙasa sun fada hannun jami’an tsaron Civil Defenc

Jami’an hukumar tsaro ta NSCDC sun tare wasu manyan motocin kaya guda biyu dake dauke da karfen digar jirgi a yankin Ooloru dake jihar Kwara.

Kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kwara, Umar Mohammed ya fadawa yan jarida a Ilorin ranar Laraba cewa an kama mutane shida dake tare da motocin biyu.

Ya kuma kara da cewa mutanen da aka kama sun tawo ne daga kauyen Jagundi a karamar hukumar Kafanchan ta jihar Kaduna.

Kwamandan ya ce a yayin kamen mutane biyu sun samu nasarar tserewa amma ya ci alwashin za su shiga hannu nan ba dadewa ba.

Tuni hukumar ta nemi umarnin kotu domin cigaba da tsare motocin da kayan ke ciki har zuwa lokacin da kotu za ta zartar da hukunci kan batun.

Da ya daga cikin mutanen da aka kama Yunusa Bello ya ce bai san kayan na sata ba ne kuma an dauke shi kwangilar tuka motar ne da zummar za a biya shi miliyan daya.

More from this stream

Recomended