Baduru Ya Maida Martani Kan Rahoton Ambaliyar Ruwa a Hadijia – AREWA News

Daga VOA Hausa

Rahotan binciken wadda kwamitin kwarru akan sauyin yanayi da sha’anin muhalli, karkashin kulawar majalisar dinkin duniya suka fitar yayi hasashen cewa, ambaliyar ruwa zata mamaye garin Hadejia baki dayan sa nan da shekaru biyu masu zuwa. Don haka, akwai bukatar mahukunta su dauki matakin sauyawa Hadejia matsugunni domin kare rayuwa da dukiyar al’umma.

Hasashen kwararrun wadda aka yi amfani da hanyoyin kimiyyar fasahar zamani, ya nuna su-ma garuruwan Auyo da Birniwa dake makwaftaka da garin na Hadejia na cikin yanayin barazanar mamaya daga ambaliyar ruwa.

Rahotan ya lura da tsananin ambaliyar data wakana a Hadeija a bara da-ma sauran garuruwa dake kan hanyar kogin Hadejia-Jama’are da kuma Komadugu zuwa tafkin Chadi.

Sai dai a karon farko gwamna Badaru Abubakar ya magantu dangane da wannan rahoto.

A wata gajeriyar kasida daya wallafa game da rahotan majalisar dinkin duniya akan makomar Hadejia, Arch. Aminu Kani yace, daukar matakan kare Hadejia daga barazanar ambaliyar ita ce mafita, amma ba sauyawa garin matsugunni ba, la’akari da dinbin kayan al’adu da kadarorin gwamnati dana daidaikun mutane na biliyoyin naira a garin Hadejia.

Sai dai gwamna Badaru na cewa, koda yake batun ne na amfani da ilimin kimiyya, amma lissafin kalkuleta ne zai fayyace matakin da gwamnati zata dauka bayan karbar rahotan kwararru akan wannan lamari.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...