Jam’iyyar Allied People’s Movement (APM) ta bayyana cewa tana da yaƙinin ɗan takararta na shugaban ƙasa, Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo, zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne bayan ta tabbatar da miƙa sunayen ‘yan takararta na shugaban ƙasa, mataimakinsa da na Majalisar Tarayya ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).
Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Abubakar Yusuf, ya ce APM na ci gaba da samun ƙarin magoya baya a sassan ƙasar, kuma tana da tabbacin samun nasara a zaɓen.
Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnatin APC da gaza magance matsalolin tsaro da tattalin arziki, tana mai cewa gwamnatin APM ƙarƙashin jagorancin Makinde za ta bai wa jin daɗin ‘yan Najeriya fifiko.
APM Ta Ce Makinde Zai Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027

