Ansaru ta dauki alhakin hari kan sarkin Potiskum – AREWA News

Kungiyar yan ta’adda ta Ansaru ta dauki alhakin kai hari kan ayarin sarkin Potiskum, Alhaji Umaru Bubaram.

An kai wa sarkin hari ne akan hanyar Kaduna zuwa Zariya.

Audu Bulama Bukarti, lauya mai fashin baki kuma mai kare hakin dan Adam shine ya bayyana haka cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya nuna cewa harin na nufin kungiyar Ansaru da aka kafa a shekarar 2012 ta kara dawowa.

Kungiyar ta fitar da sanarwar kai harin ta kafar yada labarai ta Thabat da kungiyar Al-qaida ke amfani da ita.

Wannan hari na biyu da kungiyar ta kai tun bayan wanda ta kai a shekarar 2013 a wani gida inda wasu ma’aikata yan kasashen waje na kamfanin gine-gine na Setraco suke dake garin Azare.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar ƙera bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...