Ana gumurzu da masu zanga-zanga a Abuja

A yanzu haka dai dimbin masu zanga-zanga na gudanar da zanga-zanga kan wata babbar hanya a garin Kugbo da ke Asokoro a karamar hukumar Abuja Municipal Council (AMAC).

Masu zanga-zangar wadanda suka fito a daruruwansu sun ki ja da baya duk da harbin bindiga da hayaki mai sa hawaye da jami’an tsaro suka jefa musu.

Idan ba a manta ba, wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta hana masu zanga-zanga zuwa filin wasa na Moshood Abiola. 

Amma yayin da wasu daga cikinsu suka zarce zuwa filin wasan, wasu kuma sun taru a wurare daban-daban na babban birnin kasar.

Jami’an tsaro dai na cikin tsaka mai wuya wajen shawo kan gungun matasa da ke dagewa cewa za su ci gaba da zama a kan tituna har sai an biya musu bukatunsu na inganta tattalin arziki.

Asokoro, inda masu zanga-zangar suke, ya kunshi kujerar mulkin Najeriya, cibiyoyin gwamnati, barikokin soji da kuma babban ofishin hukumar tsaro ta farin kaya (DSS).

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]