An yi arangama kan muzguna wa Musulmin China a Hong Kong

'Yan sanda na neman kama wani daga cikin masu zanga-zanga

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

‘Yan sanda na neman kama wani daga cikin masu zanga-zanga

An yi dauki ba dadi tsakanin ‘yan sanda da masu zanga-zangar goyon bayan Musulmin China a birnin Hong Kong.

Daruruwan masu zanga-zanga a Hong Kong sun yi gangamin nuna goyon baya ga Musulmi ‘yan kabilar Uighur da ake musgunawa a China.

Mutanen na zargin hukumomin China da tura dubban Musulmai ‘yan kabilar Uighur zuwa wasu sansanonin da ta kira na sake ilmantarwa.

Masu zanga-zanga da suka ce suna goyon bayan Musulmin sun kuma nuna fargabar samun kansu a irin halin da Musulman Uighur ke ciki.

Sun ce suna neman kawo karshen abin da suka kwatanta da karfa-karfar da China ke yi a gabashin Turkestan da sauran yankuna.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]