An tsaurara matakan tsaro a Daura gabanin komawar Buhari gida

An tsaurara matakan tsaro a Daura mahaifar shugaban kasa, Muhammad Buhari gabanin dawowarsa gida bayan kammala wa’adin mulkin sa.

Buhari zai sauka daga mulki a mako mai zuwa bayan kammala wa’adin mulkinsa na biyu inda zai mikawa Bola Ahmad Tinubu mulki a ranar 29 ga watan Mayu.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa tuni masarautar Daura ta shirya gudanar da gagarumar Durbar domin girmama Buhari wanda ke rike da sarautar Bayajidda II.

Masarautar ta kuma shirya karin wasu wasannin da suka haÉ—a da Kokawa, Dambe da kuma Sharo.

Har ila yau wasu gamayyar kungiyoyi da suka haÉ—a da Daura Emirate Development Association (DEDA) suma sun shirya na su bikin domin tarbar Buhari a cewar Alhaji Aliyu Daura shugaban kungiyar ta DEDA.

Jami’an tsaro sun hana shiga ko kuma shiga gidan shugaban kasar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]