An tabbatar da dakatar da Koeman wasa biyu a La Liga

Ronald Koeman

Asalin hoton, Getty Images

Ronald Koeman ba zai ja ragamar Barcelona ba a wasan La Liga ranar Asabar da za ta fafata da Atletico Madrid a Camp Nou.

Hakan ya biyo bayan rashin nasara da kungiyar ta yi , bayan daukaka karar dakatar da kocin wasa biyu da hukumar kwallon kafar Spaniya ta hukunta shi.

An kori Koeman a wasan da Granada ta doke Barcelona da ci 2-1 a Camp Nou ranar 29 ga watan Afirilu, bayan fadin kalamai na rashin da’a ga alkalin wasa mai jiran ko-ta-kwana.

Tun farko kwamitin gasar La Liga na hukumar kwallon kafar Spaniya ya dakatar da kocin wasa daya nan take daga baya ya kara hukuncin zuwa karawa biyu.

Kocin dan kasar Netherland bai ja ragamar kungiyar wasan da ta doke Valencia 3-2 a gasar La Liga ba ranar Lahadi.

Mataimakin Koeman, Alfred Schreuder shi ne zai ja ragamar Barcelona a fafatawar da za ta yi da Atletico Madrid ranar Asabar.

Barcelona tana mataki na uku a kan teburin La Liga da maki 74, iri daya da na Real Madrid wadda take ta biyu.

Atletico Madrid ce ta daya a kan teburi da maki 76, kuma saura wasa hurhudu a karkare kakar bana.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...