Atoni janar na Isra’ila ya samu Firai Minista Benjamin Netanyahu da laifin cin hanci da rashawa da kuma laifin cin amana kan tuhume-tuhume uku da ake masa.
Ana zargin Netanyahu da karbar kyaututtuka daga hamshakan ‘yan kasuwa da alfarma.
Ya dai musanta aikata ba dai-dai ba tare da cewa bi-ta-da-kulli jam’iyyar adawa ke masa da ‘yan jarida.
Netanyahu ya kafe ba zai yi murabus daga mukaminsa ba, kuma babu dokar da ta ce ya yi hakan.
- Netanyahu ya gaza kafa gwamnati, yanzu damar ta Gantz ce
- Netanyahu: Ana gab da kammala bincike kan zargin cin hanci
Sai dai sanarwar samun shi da laifin rashawar na zuwa ne yayin da kasar ke shirin tsayawa cik na kwanaki biyu sakamakon karasa zaben da ba su kammalu ba, a zaben gama gari na watan Satumba da ya wuce.
A ranar Laraba, abokin hamayyar Netanyahu wato Benny Gantz ya sanar da har yanzu ya gagara samun rinjaye a majalisa da zai ba shi damar kafa gwamnatin hadaka.
Shugaba Reuven Rivlin ya bai wa Netanyahu damar samar da gwamnatin hadaka, amma har yanzu ya gagara hakan.
A ranar Alhamis shugaba Rivlin ya bukaci ‘yan majalisa su amince da firai ministan nan da makwanni uku, don gudun sake yin zabe karo na uku cikin shekara guda.