An kashe mutane, an kona gidaje a rikicin Kazakhstan | BBC Hausa

@

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

An kashe mutum 8 tare da jikkata wasu fiye da 20 a wani tashin tashinan da aka yi a wani kauye ranar Juma’a a Kazakhstan.

Rahotanni sun ce an cinna wa gidaje da shaguna fiye da 45 wuta a lokacin rikicin kabilancin.

Rikicin ya barke ne tskanin ‘yan kabilar Dungan da Musulmai ‘yan kabilar Hui da suka yi gudun hijira daga China a cikin karni na 19.

Shugaban kasar Kassym-Jomart Tokayev ya ce ‘yan sanda na tsare da 47 da ake zargi ssuna da hannu a fadace-fadacen da ake yawan samu tsakanin mazauna yankin.

Shugaban Kassym-Jomart ya shaida wa ‘yan jarida cewa kura ta lafa, kuma ya umurci jami’an tsaro da su dauki matakan hana sake aukuwar hakan.

Ya ce jami’an tsaron za su gurfanar da masu yada labarun karya da kalaman nuna tsana da na tunzura a gaban kotu.

Hotunan rikicin da aka yada a kafafen zumunta a ranar Juma’a sun nuna wasu matasa dauke da makamai na cinna wuta a kan gine-ginen da ke kan hanyar kauyen.

Ministan yada labaran kasar ya ce rikicin na da nasaba da fadace-fadacen da ake samu a yankin.

More News

Wani mutumi ya yi garkuwa tare da kashe Æ´ar’uwarsa a Kaduna

A ranar Lahadin ne mazauna birnin Zariya na jihar Kaduna suka shiga alhini cikin alhini sakamakon kama wani mai suna AbdulAzeez Idris da ake...

ÆŠan ta’addar Boko Haram ya miÆ™a kansa ga sojoji

Alhaji Wosai wani mamba a ƙungiyar ƴan ta'addar Boko Haram ya miƙa kansa ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai. Rahotanni sun bayyana...

An kuÉ“utar da wasu É—aliban da aka sace a jami’a a Kogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta bayyana cewa an ceto 14 daga cikin daliban jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara Okene...

Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar...