Akwai yiwuwar United za ta kori Soskjaer, PSG na shirin kawo Aubameyang | BBC Hausa

Ole Gunner Soskjaer
Image caption

Ana tunanin maye gurbin Soskjaer da Gareth Southgate

Tottenham na kokarin kammala wata yarjejeniyar dawowa da tsohon dan wasanta Gareth Bale daga Real Madrid kafin a rufe kofar cinikin yan wasa.(Express).

Manchester United za ta iya raba gari da mai horar da ‘yan wasanta Ole Gunner Soskjaer, matsawar ba a samu wani sauyi ba ga sakamakon wasanni masu zuwa.

Wata majiya na cewa tuni an fara neman kociyan tawagar kwallon kafa ta Ingila Gareth Southgate a matsayin madadinsa.(Mail).

Barcelona ta dakata da neman dan wasan gaban Arsenal Pierre-Emerick Aubameyang a kakar bana, inda za ta mai da hankali kan dan wasan gaban Valencia Rodrigo Moreno(Sport).

A wata mai kama da haka PSG za ta ci gaba da neman Pierre-Emerick Aubameyang kafin a rufe kofa domin maye gurbin Edinson Cavani.(Foot Mercato – in French).

Rahotanni na cewa Atletico Madrid na shirin kasa Manchester United da Chelsea wurin sayen Edinson Cavani na PSG.(Goal.com).

An ruwaito cewa dan wasan ya bayyana Atletico Madrid a matsayin kungiyar da ya zabi ya koma da buga wasa.

Ita kuwa Arsenal ta na dab da kammala sayen mai tsaron bayan Flamengo na Brazil Pablo Mari.(Mail).

Har yanzu Manchester United na da sha’awar sayen Bruno Fernandez duk da cewa sun kasa cimma farashin da Sporting Lisbon ta sa kansa.(A Bola – in Portuguese).

Wasu rahotanni na cewa mai horar da Tottenham Jose Mourinho ya soki Inter kan shirinta na raba kungiyarsa da dan wasan tsakiyarta Christian Eriksen.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...