Aisha Buhari Ta Caccaki Jami’an Tsaron Najeriya | VOA Hausa

Uwargidan shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta yi kira ga hukumomin jami’an tsaron kasar da su yi gaggawar magance matsalar tsaron ‘yan bindiga da ta addabi wasu sassan Najeriya.

Rahotanni da dama sun ruwaito cewa, Aisha ta yi kiran ne, a yau Asabar yayin da ta kai ziyara jihar Katsina domin raba kayan tallafi ga wadannan hare-haren ‘yan bindiga ya shafa.

Yankin karamar hukumar Batsari, na daga cikin yankunan da suka yi fama da hare-haren ‘yan bindiga a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Aisha ta ce, lokaci ya yi da ko a kawo karshen ‘yan bindigar, in ba haka, su ‘yan bindigar za su kawo karshen mutane.

Uwargidan shugaban kasar, ta kuma kalubalanci duk masu karfin fada a ji, da su fito su fadi abubuwa da suke faruwa marasa dadi a Najeriya, domin mahukunta su dauki mataki akai.

Ba dai yau Aisha ta fara sukar lamirin gwamnatin mijinta ba, ko a ‘yan kwanakin nan wasu rahotanni sun ruwaito ta tana sukan matakin kashe dala miliyan 16 wajen sayen gidan ragar sauro.

A kuma shekarun baya, ta taba fitowa ta soki gwamnatin mijinta, inda ta yi korafin cewa wasu mutane kalilan sun karbe ragamar tafiyar da gwamnati, kalaman da shi kansa Buharin ya musanta.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...