A Sake Kaiwa Tawagar Gwamnan Borno Hari

Majiyun Muryar Amurka sun bayyana cewa, gwamnan ya je Baga ne domin ci gaba da shirye shiryen maida ‘yan gudun hijira zuwa garuruwansu na asali, wadanda kungiyar Boko Haram ta raba da muhallansu tun 2014, bayan kafa kwamitin makonni biyu da suka gabata, karkashin jagorancin kwamishinan ma’aikatar shari’a na jihar Barrister Kaka Shehu Lawan.

Bisa ga majiyun harin bai hana gwamnan da tawagarsa isa Baga ba, inda suka kwana domin ci gaba da wannan shiri.

gwamnatin-barno-za-ta-maida-yan-gudun-hijran-baga-mazauninsu

gwamnatin-borno-ta-fara-maida-yan-gudun-hijira-gida

zulum-ya-ce-harin-da-aka-kai-kan-tawagarsa-zagon-kasa-ne

Shi dai gwamnan ya tafi Baga ne ta jirgi mai saukar angulu yayinda tawagar tasa suka tafi ta hanyar mota.

Maharan da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar Boko Haram ne, sun kai wa tawagar harin ne a kauyen Cross Kawa da ke kusa da barikin sojan hadin guiwa da ya kunshi sojojin kasashen Chadi, Kamaru, da Nijar.

Idan ba a manta ba, kwanaki hudu da suka gabata, aka kaiwa jami’an sojoji hari a Damboa aka kashe babban kwamandan soja na garin Kanar Dahiru Bako.

Wannan ne karo na biyu da ake kaiwa tawagar gwamna Babagana Zulum hari cikin shekara guda.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...