

Ibrahim Idris, tsohon gwamnan Jihar Kogi, ya rasu yana da shekaru 77.
Jaridar TheCable ta fahimci cewa tsohon gwamnan ya rasu ne a ranar Lahadi a ƙasar Birtaniya.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa babarai na jihar Kogi, Kingsley Fanwo, ya sanya wa hannu, Gwamnan jihar Usman Ododo ya ce “mutuwa ta raba jihar ɗanta na asali da ya sadaukar da wani ɓangare mai muhimmanci na rayuwarsa wajen yi wa al’umma hidima.”
Fanwo ya ce Ododo ya ayyana kwanaki uku na zaman makoki domin girmama Idris, tare da umarnin yin ƙasa da tutar Najeriya ya zuwa rabin sanda a lokacin.
Ododo ya bayyana cewa jihar Kogi ta samu ci gaba da gina cibiyoyi a lokacin mulkin Idris.
“Gwamnan ya kuma ayyana cewa za a yi wa tsohon gwamnan ban girma, inda gwamnatin Kogi za ta ɗauki nauyin dukkan kuɗin jana’iza tare da shirya duk abin da ya dace don ba shi girmamawar da ta dace da ta da ce da matsayin tsohon gwamna,” in ji sanarwar.
“Gwamna Ododo ya lura cewa gwamnatin tsohon gwamna ta yi muhimman ayyuka a fannin gine-gine, ilimi, kiwon lafiya da sauran muhimman fannoni, inda tasirin mulkinsa zai ci gaba da kasancewa wani ɓangare na tarihin ci gaban Jihar Kogi.
An haifi Idris a ranar 6 ga Afrilu, 1949. Ya yi gwamnan Jihar Kogi daga 2003 zuwa 2012. Ya lashe zaben gwamna na 2003 a karkashin jam’iyyar PDP.
Ya kuma lashe zaben gwamna na 2007, amma kotun zabe ta soke nasararsa saboda sunan da hoton Abubakar Audu na jam’iyyar ANPP ba su shiga takardar zabe ba.