
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce ‘yan Najeriya za su fara ganin raguwar kudin sufuri daga ranar 1 ga Oktoba 2026, karkashin shirin National Affordable CNG Transit Programme na amfani da iskar gas din CNG wajen samar da sufuri mai saukin kudi.
Tinubu ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, inda ya ce ya gana da gwamnonin jihohin kasar 36 a ranar 27 ga Agusta, inda suka amince da samar da hanyoyin rage kudin sufuri.
Shugaban ya ce an kafa kwamitin aiwatar da shirin karkashin inuwar Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF), karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq.
Ya ce kwamitin, tare da shirin PI-CNG & EV, gwamnatocin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki, suna aiki wajen gano hanyoyin sufuri da ya kamata a fara amfani da matakan rage farashi, tare da samar da abubuwan da ake bukata domin aiwatar da shirin.
Tinubu ya ce wasu jihohi sun riga sun fara ganin saukin kudin sufuri sakamakon amfani da motocin CNG da na lantarki. Ya bayar da misalin Jihar Borno, inda ya ce wasu motocin sufuri masu amfani da CNG da lantarki na jigilar fasinjoji kan farashin N50 zuwa N100, a hanyoyin da masu sufuri na kasuwanci ke karbar N300 zuwa N600.
Ya kuma ce a Kaduna, motocin bas 100 masu amfani da CNG suna jigilar mutane kyauta a wasu manyan hanyoyi, yayin da a Oyo aka rage kudin sufuri tsakanin Legas da Ibadan daga kusan N8,000 zuwa N3,200 a farkon amfani da motocin CNG.
Shugaban ya ce fiye da motoci 120,000 aka riga aka sauya su zuwa amfani da CNG a fadin Najeriya, yayin da ake da cibiyoyin sauya motocin zuwa CNG sama da 400 da kuma tashoshin cike CNG sama da 90.
Ya bukaci gwamnatocin jihohi da su kara saurin aiwatar da shirin kafin ranar 1 ga Oktoba, tare da yin aiki da kungiyoyin masu sufuri da masu motocin haya domin tabbatar da cewa rage kudin makamashi ya bayyana kai tsaye a farashin da fasinjoji ke biya.
Tinubu ya ce matsalar makamashi da ake fuskanta a duniya ta kara muhimmantar da bukatar fadada hanyoyin samar da makamashi masu rahusa, yana mai cewa Najeriya na da iskar gas da za ta iya taimakawa wajen rage dogaro da farashin man fetur.
Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da tallafa wa jihohi wajen fadada kayayyakin more rayuwa na CNG da kuma karfafa sauya motocin zuwa amfani da wannan makamashi.