Jami’in NDLEA Ya Nutse A Kogin Ethiope Yayin Da Yake Bin Sawun Masu Laifi



Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta rasa wani jami’inta bayan ya nutse a Kogin Ethiope yayin da yake bin wasu mutane da ake zargi da aikata laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi a Obiaruku, karamar hukumar Ukwuani ta Jihar Delta.

Wani jami’in kuma ya tsira daga nutsewar, amma an garzaya da shi asibiti domin samun kulawar likita.

Lamarin ya faru ne yayin da jami’an ke kokarin cafke wani da ake zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi, wanda ya tsere ya shiga kogin yayin da ake kokarin kai shi wajen gadar Kogin Ethiope.

Jami’an da ke binsa sun shiga cikin kogin domin kamo shi. Sai dai daya daga cikinsu ya nutse, yayin da aka ceto dayan tare da kai shi asibiti.

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce wanda ake zargin da sauran mutanen da ake binsu sun tsere ta cikin kogin.

Majiyoyin yankin sun kuma ce an gudanar da wasu al’adun gargajiya da ake yi a Obiaruku kafin a mika gawar jami’in ga hukumomin da abin ya shafa. An ce daga cikin abubuwan da aka tanada akwai akuya da wasu kayayyaki.

Majiyoyin NDLEA sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za a gudanar da cikakken bincike domin gano yadda lamarin ya faru.

Kakakin ’Yan Sandan Jihar Delta, Bright Edafe, shi ma ya bukaci jama’a da su kwantar da hankula yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...