
Wani da ya tsira daga mutuwar dimbin mutanen da ake zargi da aikin hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a hannun Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC) a Minna, Jihar Neja, ya zargi jami’an hukumar da fesa wani sinadari da ba a san ko mene ne ba a cikin dakin da aka tsare su.
Mutumin, wanda ba a bayyana sunansa ba saboda dalilan tsaro, ya bayyana hakan lokacin da Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, da Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, suka gana da shi da wasu mutane biyu da suka tsira domin jin bayanansu kan lamarin.
Ya ce kusan mutane 67 ne aka tsare a cikin wani daki, inda suka rika korafin tsananin zafi tare da neman ruwa daga jami’an da ke gadinsu, amma ba a saurare su ba.
Wanda ya tsira din bai iya bayyana irin sinadarin da aka fesa ba, duk da tambayoyin da gwamna da ministan suka yi masa. Shi da sauran wadanda suka tsira sun kuma ce ba a ba su ruwa ba, yayin da aka hana iyalansu kawo musu ruwa.
Gwamna Bago ya ce binciken gawarwakin da aka gudanar a asibiti da dakin ajiye gawarwaki ya nuna cewa wasu daga cikin gawarwakin na dauke da kumfa a baki da kuma alamun jini, yayin da wasu ke da fatar jiki da ta balle.