

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 12 a Minna babban birnin jihar domin dakile karin tashin hankali da karya doka da oda.
Gwamnan ya sanar da hakan ne lokacin da ya karɓi bakuncin Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, a ziyarar ta’aziyya da ya kai jihar kan mutuwar wasu mutane 37 a lokacin da su ke tsare a hannun jami’an hukumar tsaro ta Civil Defence bayan da aka kama su a wurin haƙar ma’adanai.
Gwamnan ya ce dokar hana fitan, wadda ta fara aiki daga yau, za ta kasance daga ƙarfe 6 na yamma zuwa 6 na safe domin hana hare-hare kan kadarorin gwamnati da na masu kamfanoni masu zaman kansu da masu zanga-zanga ke yi.
Ya bayyana cewa waɗanda suka mutu suna tsakanin shekaru 14 zuwa 18.
Ya ce: “Ba mu san ainihin dalilin ba tukuna amma akwai yiwuwar abu biyu. Na farko, daga rahoton da muka samu, an kama mutane 67 aka tsare su a ofishin Civil Defence. Wasu daga cikin waɗanda suka tsira sun ce rashin iska da ƙishirwa ne ya kashe su. A zahiri, binciken asibiti da dakin ajiye gawa ya nuna cewa wasu daga cikin gawarwakin suna da kumfa a baki tare da jini da kuma fatar jiki tana ɓarewa . Saboda haka ba za mu iya kawar da yiwuwar guba ba.”
Ya kara da cewa: “An dakatar da kwamandan jihar wanda ya bayar da umarnin tsare mutanen fiye da sa’o’i 24 a cikin ɗaki ɗaya. Wannan rashin tausayi ne. Jami’an da ke bakin aiki sun ce sun ji ihun mutanen suna neman taimako amma suka yi kunnen uwar shegu.”
Bago ya ce an lalata motocin kamfanin sufuri na jihar da ofisoshin jam’iyyar APC su, yana mai cewa “’yan ta’adda sun mamaye tituna, dole ne mu dakile hakan domin samun zaman lafiya.”
Ya kuma sanar da haramta dukkan ayyukan hakar ma’adinai a jihar tare da umartar ma’aikatan su daina zuwa wuraren aiki.
Gwamnan ya roki jama’a da su yi hakuri tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta binciko ainihin dalilin faruwar lamarin domin kauce wa faruwar haka anan gaba.
Ya ce ayyukan hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba suna jawo yara su bar makaranta.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, wanda ya zo tare da Babban Kwamandan NSCDC, ya bayyana lamarin a matsayin abin bakin ciki.
Ya ce shugaban ƙasa yana cikin damuwa kan lamarin, kuma zai iya shafar ci gaban gwamnati a matakin jiha da na tarayya.
Tunji-Ojo ya tabbatar da cewa ba za a sake samun irin wannan lamarin ba, tare da alkawarin cewa za a tabbatar da adalci.