
Akalla mutane 37 da ake zargi da haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba sun mutu yayin da suke tsare a hannun Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC) a jihar Neja.
An kama mutanen ne a ƙauyukan M.I. Wushishi da Lukoto yayin samamen da jami’an hukumar suka gudanar a ranakun 15 da 16 ga Satumba 2026, a wani yunƙuri na dakile haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.
Kwamandan NSCDC na jihar Neja, Suberu Aniviye, ya ce an gano gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka tsare da sanyin safiyar 17 ga Satumba, bayan zargin barkewar wata cuta.
Ya bayyana cewa an kai gawarwakin mamatan zuwa Babban Asibitin Minna domin gudanar da gwaje-gwajen lafiya da gano ainihin musabbabin mutuwar.
Sai dai NSCDC ta ce har yanzu ba a tabbatar da wata cuta a matsayin sanadin mutuwar mutanen ba.
Kakakin Hulɗa da Jama’a na NSCDC na ƙasa, Babawale Afolabi, ya ce Kwamandan Janar na hukumar, Ahmed Abubakar, ya umarci kafa wata tawagar bincike mai ƙarfi domin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Afolabi ya ce tawagar za ta duba halin da waɗanda ake zargin suke ciki lokacin da aka kama su, tsawon lokacin da suka yi a tsare, yanayin wurin da aka tsare su da kuma irin kulawar lafiya da aka ba su.