

An gano gawar Ayodele Odularu, wata ƴan Najeriya malamar Jami’ar Fort Hare, Afirka ta Kudu, a gidanta da ke lardin Eastern Cape.
Yayanta, Gbadebo Odularu, ya shaida wa jaridar Punch’s Diaspora Tales a ranar Laraba cewa ta rasu a ranar 16 ga Agusta tana da shekaru 51.
Wani ɗan uwan marigayiyar da ya nemi a ɓoye sunansa ya bayyana cewa mutuwar ba ta kasance ta haka kawai ba , kuma iyalan har yanzu ba su fahimci cikakken yanayin lamarin ba. Sun nemi a gudanar da bincike kan mutuwar.
A cikin sanarwar neman taimakon kuɗin a shafin GoFundMe da Gbadebo ya wallafa a madadin iyalan, an bayyana marigayiyar a matsayin wadda “ta sadaukar da rayuwarta wajen neman ilimi, bincike, da kuma samar da kyakkyawar makoma ga al’umma.”
Iyalan sun ce: “Ko da rayuwarta a duniya ta kare da wuri, tasirin rayuwarta ya ci gaba ta hanyar mutanen da ta zaburar, ilimin da ta yada, da al’ummomin da ta yi fatan yi wa hidima.”
Sanarwar ta kara da cewa: “Ayodele ba kawai ’yar uwa ba ce. Ta kasance ’ya abar ƙauna abokiya, malama, mai ba da shawarwari, kuma tushen ƙarfafawa, tausayi, hikima da ƙarfin zuciya ga duk wanda ya san ta.”
“Kansacewarta a wuri na kawo annashuwa. An san ta da kyautatawa, dariya mai ɗaukar hankali, karamci, juriya, da sadaukarwa wajen ɗaga darajar wasu. Ta kasance da baiwa ta musamman wajen sa mutane su ji darajarsu, a saurare su, kuma su zabura.”
“Dr. Ayodele Odularu ta sadaukar da rayuwarta wajen neman ilimi, bincike, da kuma samar da kyakkyawar makoma ga al’umma. A matsayinta na Babbar Mai Bincike mai zaman kanta a Jami’ar Fort Hare, ta bayar da muhimmiyar gudummawa ga binciken ilimi da ci gaban sani ta hanyar ayyukan bincikenta.”
A ranar Alhamis, Jami’ar Fort Hare ta shirya taron tunawa da marigayiyar.
Mutuwar ta na zuwa ne a daidai lokacin da ake kai hare-hare masu tayar da hankali kan ’yan Najeriya da sauran ’yan Afirka dake zaune a ƙasar ta Afirka ta Kudu.