
Masu garkuwa da mutane da suka sace malamai guda shida a Jihar Zamfara sun nemi kudin fansa har naira miliyan 30 kafin su sako su kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Wani mazaunin kauyen Dakko a karamar hukumar Bakura, Malam Muhammad Ibrahim, ya tabbatar wa da jaridar ta Daily Trust lamarin a sanarwar da aka yi da shi ta wayar tarho.
Ibrahim ya ce direban malamai, wanda aka sace su tare, an sake shi bayan an biya kudin fansa na naira miliyan 2.
Ya ce, “’Yan bindigar sun sace mutane takwas malamai biyar, direbansu, da kuma wasu mutane biyu da aka sace a hanyarsu ta dawowa daga gona.
Mun ji cewa ’yan bindigar sun nemi naira dubu 300 kowanne da kuma jarkoki biyu na lita 25 na man fetur a matsayin kudin fansa ga mutanen da aka sace daga gona. Amma ga direban, sun karɓi naira miliyan 2 daga iyalansa.
Direban ya samu ’yanci yau (Asabar) kuma ya koma gida cikin iyalansa a kauyen Kwatsama. Haka kuma mun ji cewa ana shirin biyan naira miliyan 30 domin a sako malamai.”
Ya kara da cewa wani Sanata daga Jihar Zamfara ya yi alkawarin biyan kudin fansa domin a sako malamai. “Muna fatan hakan ba zai jinkirta ba.”
Ibrahim ya roki hukumomi da su kara kaimi wajen ceto malaman, yana mai nuna damuwa cewa saboda tsufansu, jinyar da suke yi a hannun ’yan bindiga na iya shafar lafiyarsu.
“Malaman tsofaffi ne, kuma kasancewarsu a hannun ’yan bindiga kadai na iya jawo matsalar lafiya. Gwamnati ta gaggauta ceto su,” in ji shi.
Wani ɗan ɗaya daga cikin malamai da aka sace, wanda bai so a bayyana sunansa ba, ya ce iyalan sun yi farin ciki da wannan sabon ci gaba.
“Wannan ci gaban ya kara mana kwarin gwiwa kan dawowar iyayenmu da sauran malamai,” in ji shi.
Ya tabbatar da cewa ’yan bindigar sun nemi Naira miliyan 30 domin a sako malamai.
“Mun yi fatan za a iya tara kudin kafin wa’adin da ’yan bindigar suka bayar ya kare,” in ji shi.
Yan bindigar sun yi garkuwa da Malaman a lokacin da su ke kan hanyarsu ta dawowa daga taron addu’a da aka shirya wa shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu.
