

Gbenga Olawepo-Hashim dan takarar shugaban kasa a ƙarƙashin jam’iyar Accord ya ce za a iya sayar da man fetur kan ₦605 kowace lita idan aka zabe shi ya zama shugaban ƙasar Najeriya.
A ranar 26 ga watan Mayu ne, Olawepo Hashim ya sanar da aniyarsa ta tsaya takarar shugaban kasa a ƙarƙashin jam’iyar Accord.
Amma kuma a cikin watan Yuni jam’iyar ta Accord ta barranta kanta daga Olawepo-Hashim wanda tsohon jigo ne a jam’iyar adawa ta PDP a cikin wata sanarwa da jam’iyar ta fitar ta ce bata gudanar da zaben fitar da gwani ba ballantana har ta tsayar da ɗantakara a zaɓen shugaban ƙasar na 2027 inda ta ce ƙarya ce tsagoronta rahoton dake cewa Olawepo-Hashim shi ne ɗantakara.
Duk da haka Olawepo-Hashim ya cigaba da yakin neman zabe tare da gabatar da kansa a matsayin ɗantakarar shugaban ƙasa na jam’iyar.
A wata tattaunawa da ya yi yan jaridu ya ce daga bisani man yana iya saukowa kasa da haka matukar abubuwa suka dai-dai ta musamman musayar kuɗin ƙasashen waje.
Olawepo-Hashim ya ce za a iya sayar da man akan farashin haka ba tare da raguwar kuɗin dake shiga aljihun gwamnati da kuma wanda ke shiga asusun rabon arzikin ƙasa.
Ya ce kamata ya yi a mayar da hankali wajen tantance ainihin abin da ake kashewa hakowa tare da tacewa da kuma rarraba man fetur a maimakon a riƙa kwatanta farashin man fetur ɗin na kasuwar duniya.