

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bukaci a gaggauta kama shugaban ƙaramar hukumar Kuje, Mista Samuel Danjuma Shekwolo , bisa ga furucinsa na cewa dole ne mazauna yankin su zaɓi jam’iyar APC ko kuma su bar yankin karamar hukumar.
Jam’iyyar adawar ta bayyana wannan mataki a matsayin “barazanar tilastawa mutane yin ƙaura” wanda hakan ya keta sashe na 40, 41 da 42 na kundin tsarin nulkin Najeriya.
A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta, an ji shugaban ƙaramar hukumar yana cewa “Na ce a cikin karamar hukuma ta, ko dai kana yin APC ko ka bar karamar hukumar. Ba zan yi jayayya da kai ba”.
Da take mayar da martani kan batun, a cikin wata sanarwa da ta fitar, sakataren yaɗa labarai na ƙasa na ADC, Mallam Bolaji Abdullahi, ya danganta wannan furuci da makamancinsa da Sanata Francis Fadahunsi na APC ya yi har ta kai ga yi masa tambayoyi a hannun ƴan sanda kuma aka sake shi ba tare da tuhuma ba duk da barazanar da ya yi wa ƴan adawa masu jefa ƙuri’a a lokacin zaɓen gwamnam Osun.
ADC, yayin da take danganta maganganun da maganar shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi ranar 29 ga Yuli dake cewa “ Komai aka yi dai-dai ne a siyasa,” inda ta bukaci shugaban ƙasar da kansa ya bayyana ma’anar maganarsa kuma ya yi kira ga jam’iyyarsa zuwa ga oda.
Jam’iyar ta ADC ta shawarci kwamitin samar da zaman lafiya na ƙasa da ya yi tun da wuri inda ta yi gargadin cewa idan aka kira har sai 2027 to kwamitin zai samu kansa yana fitar da sakon ta’aziya mai makon rokon a zauna lafiya.
Har ila jam’iyar ta yi kira ga hukumar tsaro ta farin kaya DSS da kuma babban sifetan yan sandan Najeriya da su kama Mr Sokwolo kana su gurfanar da shi a gaban kotu kamar yadda doka ta tanada.