Danjuma Goje ya sha kaye a zaɓen fitar da  gwani na jam’iyar APC

Tsohon gwamnan jihar Gombe, Sanata Muhammad Danjuma Goje ya ya sha kaye a zaɓen fitar da gwani da jam’iyar APC ta gudanar a mazaɓarsa ta Gombe ta Tsakiya.

Hakan na nufin Sanatan ya rasa tikitin tsayawa takara a ƙoƙarinsa na tsayawa zaɓe a karo na biyar domin wakiltar al’ummar yankin nasa.

A zaɓen kato bayan kato da aka gudanar ranar Litinin a ƙananan hukumomin Akko da kuma Yamaltu Deba da mazaɓar majalisar datttawan ta kunsa ya nuna cewa DCP Muhammad Ahmed mai ritaya ne ya samu nasarar lashe zaɓen da gagarumin rinjaye.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen, Dr Habu Dahiru ya ayyana cewa DCP Ahmad ya samu kuri’a 42785  a yayin da Sanata Goje ya samu kuri’a 10425.

Tun da farko, Ahmad masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC suka tsayar a matsayin ɗantakarar maslaha amma Goje ya hau kujerar naƙi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]