Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa duk da ƙalubalen tattalin arziki, farashin man fetur a Najeriya ya fi na Kenya da wasu ƙasashen Afirka sauƙi.
Ya faɗi hakan ne a ranar Alhamis yayin wata ziyara da ya kai Yenagoa domin ƙaddamar da ayyuka. Shugaban ya amince cewa hauhawar farashin mai na matuƙar damun ‘yan Najeriya a halin yanzu.
Tinubu ya ce yana sane da korafe-korafen jama’a kan tsadar rayuwa, amma ya jaddada cewa Najeriya na cikin yanayi mafi alheri idan aka kwatanta da wasu ƙasashen nahiyar.
Bayanan da aka tattara sun nuna cewa a watan Afrilu na 2026, farashin mai a Kenya ya kai dala $1.37 kan kowace lita, wanda ya yi daidai da kusan N1,862.
A Najeriya kuwa, farashin mai ya kai tsakanin N1,290 zuwa N1,350 kan kowace lita, bayan tashin farashi da ya biyo bayan rikicin ƙasa da ƙasa da ya shafi Iran, Amurka da Isra’ila, wanda ya janyo hauhawar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.
Tinubu Ya Ce Farashin Mai A Najeriya Ya Fi Na Wasu Ƙasashen Afirka Sauƙi

