An ji jerin manyan fashe-fashe a birnin Erbil, babban birnin yankin Kurdistan da ke arewacin Iraq, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin fargaba.
Rahotanni sun ce fashe-fashen sun auku ne a kusa da filin jirgin saman Erbil, inda dakarun ƙawancen ƙasashen duniya da Amurka ke jagoranta ke da sansani na soja.
Rundunar sojin Iraki ta bayyana cewa ta kakkaɓo wani jirgi marar matuƙi da aka harba zuwa ofishin jakadancin Amurka da ke birnin. Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.
Yankin Kurdistan na ɗauke da ƙungiyoyin Kurdawa da dama, kuma wasu daga cikinsu na adawa da gwamnatin Iran, abin da ke ƙara tsananta yanayin siyasa a yankin.
Haka kuma, akwai rahotannin da ke cewa shugaba Donald Trump ya yi waya da shugabannin Kurdawa a wannan makon. Rahotannin sun ce ya shawarce su su tayar da bore domin hambarar da gwamnatin Iran. Ba a samu wata sanarwa a hukumance daga ɓangarorin da abin ya shafa ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Manyan Fashe-Fashe Sun Girgiza Erbil A Arewacin Iraq

