Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin wutar lantarki a wuraren kwanansu.

Daliban sun kulle kofar makarantar, suna rera wakokin hadin kai tare da nuna kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar, ‘Babu hasken da za a jika Garri’ da “Ba mu da SUG” yayin da wasu kuma suka rike bokitin da babu ruwa a ciki domin nuna rashin ruwa a makarantar. 

Daliban sun koka da yadda lamarin ya janyo musu wahalhalu da kuma illa ga ayyukansu na neman ilimi.

Haka kuma an kulle da yawa daga cikin ma’aikata da shugabannin jami’ar a wajen kofar makarantar, inda aka hana su shigowa.

Sai dai babban jami’in kula da harkokin dalibai na Jami’ar, Farfesa Christopher Piwuna, ya tabbatar da kalubalen karancin ruwa da kuma katsewar wutar lantarki a gidajen daliban.

Ya kuma ɗora alhakin lamarin a kan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Jos a kan wani bashin da yake bi.

More from this stream

Recomended