Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin wutar lantarki a wuraren kwanansu.

Daliban sun kulle kofar makarantar, suna rera wakokin hadin kai tare da nuna kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar, ‘Babu hasken da za a jika Garri’ da “Ba mu da SUG” yayin da wasu kuma suka rike bokitin da babu ruwa a ciki domin nuna rashin ruwa a makarantar. 

Daliban sun koka da yadda lamarin ya janyo musu wahalhalu da kuma illa ga ayyukansu na neman ilimi.

Haka kuma an kulle da yawa daga cikin ma’aikata da shugabannin jami’ar a wajen kofar makarantar, inda aka hana su shigowa.

Sai dai babban jami’in kula da harkokin dalibai na Jami’ar, Farfesa Christopher Piwuna, ya tabbatar da kalubalen karancin ruwa da kuma katsewar wutar lantarki a gidajen daliban.

Ya kuma ɗora alhakin lamarin a kan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Jos a kan wani bashin da yake bi.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...