Ƴan bindiga sun kashe mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da kisan mutane shida da wasu ‘yan bindiga suka yi a karamar hukumar Faskari a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Aliyu, ya tabbatar da kisan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Ya ce, an kuma jikkata mutane 10 a harin wanda ya auku a kauyen Nasarawa ranar Lahadi.”

“A ranar 19 ga watan Fabrairu da misalin karfe 11:30 na dare wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne, dauke da muggan makamai irin su AK-47, sun kai hari kauyen Nasarawa, dake karamar hukumar Faskari.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]