Abdulkarim Chukkol ya kama aiki a matsayin shugaban rikon EFCC

Abdulkarim Chukkol daraktan gudanarwa a hukumar EFCC mai yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ya kama aiki a matsayin shugaban riko na hukumar.

A ranar Laraba ne shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da shugaban hukumar, Abdulrashid Bawa ya kuma bada umarnin a bincike shi kan yadda ya jagoranci hukumar.

Daga bisani hukumar DSS ta gayyaci Bawa inda ya amsa tambayoyi kan wasu batutuwa.

A wata sanarwa ranar Alhamis hukumar ta ce Chukkol na daga cikin ma’aikatan da aka kafa hukumar da su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]