Fursunoni 153 sun tsere daga gidan yarin Koton Karfe

Prisoners

Hukumar kula da gidajen yari a jihar Kogi a Najeriya, ta ce tuni ta samu zarafin cafke fursunoni 31 daga cikin 153 da suka tsere daga gidan yarin garin Koton Karfe na jihar Kogi.

Da misalin karfe 5:00 na safiyar ranar Litinin ne dai fursunonin suka tsinke bayan da ruwa kamar da bakin kwarya ya rusa wani bangare na ginin gidan yarin.

To sai dai mai magana da yawun hukumar, DSP Williams Obe Aya, ya shaida wa BBC cewa bayan tserewar fursunonin ne hukumar ta nemi daukin wasu hukumomi da ‘yan banga domin shawo kan fusrsunonin.

DSP Williams ya kara da cewa kawo yanzu jami’an nasu bisa hadin gwiwar ‘yan sintiri sun samu nasarar cafke mutum 31, kuma tuni aka mayar da su gidan yarin.

Sai dai ya ce jami’an nasu na ci gaba da farautar ragowar fursunoni 122 wadanda suka bazama daji.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]