
Kokarin da gwamnatocin kasashe da dama ke yi na kawo ƙarshen tsadar rayuwa da al’ummominsu ke fuskanta ya gamu da tasgaro a yayin da farashin danyen man fetur ya yi sama a kasuwar duniya sakamakon sake tsunduma cikin rikici da kasashen Amurka da Iran su ka yi.
Saurin dagawar farashin man da aka samu ya na zuwa ne a dai-dai lokacin da ƙasashe ciki har da Najeriya ke lalubo hanyoyin da za su ragewa mutane da da kuma kamfanonin nauyin tsadar da man fetur ya yi.
Tashin farashin ɗanyen man fetur na da alaƙa kai tsaye da farashin tatattacen ɗanyen mai irinsu man fetur, disal, kananzir da dangoginsa.
Sabon rikicin da aka samu a yankin na gabas ta tsakiya ya jawo fargabar cewa rikicin zai kawo tsaiko da man da ake fitarwa daga yankin gabas ta tsakiya ta mashigin ruwan Hormuz.
Faranshin ɗanyen man fetur nau’in Brent ya tashi ya zuwa dalar Amurka 79 kan kowace ganga kafin daga bisani ya koma dala 78.
A baya dai bayan rattaba hannu akan yarjejeniyar fahimtar juna a tsakanin Amurka da Iran farashin man ya yi kasa da dalar Amurka 70 kan kowace ganga.

