Jami’an SafeCity Security Service tare da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan jihar Delta sun kama fitaccen ɗan bindiga da ake nema, Abubakar Usman, bayan sun gudanar da wani samame a dajin Ogwashi-Uku/Adonta.
Kamen ya biyo bayan ceto wata mata mai suna Blessing Chiedu, wadda aka sace a ranar 2 ga Yuli, 2026, tare da neman kudin fansa na Naira miliyan 100. Bayan ceto ta cikin koshin lafiya, jami’an tsaro sun ci gaba da farautar masu garkuwar, inda suka yi musayar wuta da su. An kama Abubakar Usman, yayin da sauran mambobin kungiyar suka tsere cikin daji da makamansu. Bincike ya nuna cewa kungiyar tana da hannu a hare-haren sace mutane da karbar kudin fansa a yankunan Igbodo, Umunede da sauran al’ummomin da ke makwabtaka.
An Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Abubakar Usman a Jihar Delta

