An Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Abubakar Usman a Jihar Delta



Jami’an SafeCity Security Service tare da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan jihar Delta sun kama fitaccen ɗan bindiga da ake nema, Abubakar Usman, bayan sun gudanar da wani samame a dajin Ogwashi-Uku/Adonta.

Kamen ya biyo bayan ceto wata mata mai suna Blessing Chiedu, wadda aka sace a ranar 2 ga Yuli, 2026, tare da neman kudin fansa na Naira miliyan 100. Bayan ceto ta cikin koshin lafiya, jami’an tsaro sun ci gaba da farautar masu garkuwar, inda suka yi musayar wuta da su. An kama Abubakar Usman, yayin da sauran mambobin kungiyar suka tsere cikin daji da makamansu. Bincike ya nuna cewa kungiyar tana da hannu a hare-haren sace mutane da karbar kudin fansa a yankunan Igbodo, Umunede da sauran al’ummomin da ke makwabtaka.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]