2027: PRP Ta Tantance ‘Yan Takara Uku Na Shugabancin Najeriya

Jam’iyyar adawa ta PRP a Najeriya ta tantance mutum uku da za su nemi tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar.

Wata sanarwa daga sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishaq, ta bayyana cewa sama da ‘yan takara dari biyu da sittin ne ke neman muƙamai daban-daban a zaɓukan fidda gwani na jam’iyyar.

Waɗanda aka tantance domin neman tikitin shugabancin ƙasa sun haɗa da Dr. Nnaoke Ufere daga jihar Abia, Engr. (Dr.) Yakubu Mohammed Kingsley daga jihar Edo, da kuma Donald Duke, tsohon gwamnan jihar Cross River.

Jam’iyyar ta ce za ta gudanar da zaɓukan fidda gwani a faɗin ƙasar a ranar Litinin, 25 ga Mayu, 2026.

More from this stream

Recomended