2023: Matasan Arewa suna son Dangote da sauran masu kuɗi su fito takarar shugabanci a Najeriya

Wata ƙungiyar matasan arewacin Najeriya mai suna Arewa Youth Assembly sun yi kira ga hamshaƙin ɗan kasuwa, wato Alhaji Aliko Dangote, da ya fito takarar shugabancin Najeriya a 2023.

Matasan ba a nan suka tsaya ba, sun mika kiraye-kirayen nasu har zuwa ga Mr. Femi Otedola da kuma tsohuwar ministar kudin Najeriya Ngozi Okonja-Iweala.

A cewar matasan, sun yi wannan kira ne saboda ganin irin nasarorin da waɗannam mutane ne suka samu a harkar kasuwancinsu.

Don haka ya kamata su zo su gwada sa’arsu don ceto Najeriya daga halin ni-ƴasu da ta shiga a shekarun baya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]