2023: Matasan Arewa suna son Dangote da sauran masu kuɗi su fito takarar shugabanci a Najeriya

Wata ƙungiyar matasan arewacin Najeriya mai suna Arewa Youth Assembly sun yi kira ga hamshaƙin ɗan kasuwa, wato Alhaji Aliko Dangote, da ya fito takarar shugabancin Najeriya a 2023.

Matasan ba a nan suka tsaya ba, sun mika kiraye-kirayen nasu har zuwa ga Mr. Femi Otedola da kuma tsohuwar ministar kudin Najeriya Ngozi Okonja-Iweala.

A cewar matasan, sun yi wannan kira ne saboda ganin irin nasarorin da waɗannam mutane ne suka samu a harkar kasuwancinsu.

Don haka ya kamata su zo su gwada sa’arsu don ceto Najeriya daga halin ni-ƴasu da ta shiga a shekarun baya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]