Ƴansanda sun kama mutumin da ya daɓa wa matarsa wuƙa har lahira a Adamawa

Ƴan sandan jihar Adamawa sun kama wani magidanci mai suna Ibrahim Abubakar dan shekara 33 da haihuwa da ke zaune a unguwar Sabon Gari-Futy a karamar hukumar Girei da laifin daba wa matarsa Hajara Sa’adu ‘yar shekara 25 wuka har lahira.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka ba wa manema labarai a ranar Talata.

A cewar sanarwar, “Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa a ranar 8 ga Afrilu, 2024, ta kama wani mutum mai shekaru 33 da laifin kashe matarsa Hajara Sa’adu mai shekaru 25 da haihuwa.

“An kama wanda ake zargin ne biyo bayan rahoton da mahaifin marigayiyar ya gabatar wa ‘yan sanda da kuma binciken farko da aka gudanar wanda ya kai ga gano bayanan kayan aiki a wurin da laifin ya faru wanda ke da alaka da shi.“

Yan sandan dai na ci gaba da gudanar da bincike kam lamarin.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...