Ƴanbindiga Sun Sace Daliban JAMB 14 A Jihar Benue

Wasu ƴanbindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta jarrabawar shiga jami’a (JAMB) a jihar Benue, lamarin da ke ƙara nuna matsalar tsaro a ƙasar.

Rundunar ƴansandan jihar ta tabbatar da cewa an sace fasinjoji 14, ciki har da ɗaliban da abin ya shafa.

Da yake jawabi ga manema labarai, kwamishinan ƴansandan jihar, Ifeanyi Emenari, ya ce an tura jami’an tsaro zuwa yankin domin ceto waɗanda aka sace.

Lamarin ya faru ne a daidai lokacin da aka fara rubuta jarrabawar JAMB a ranar Alhamis a faɗin ƙasar.

Rahotanni sun ce an sace ɗaliban ne bayan da ƴanbindigar suka tare motar da suke ciki a kan hanyar Makurɗi zuwa Otukpo da misalin ƙarfe 8 na dare, inda suka kwace musu kayayyaki kafin daga bisani su tafi da su cikin daji.

More from this stream

Recomended