Ƴan bindiga sun kai hari ƙauyen Kuda-Kuda da ke ƙaramar hukumar Goronyo a jihar Sokoto, inda suka kashe babban limamin ƙauyen, Liman Audu, tare da wasu mutum uku.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka kashe sun haɗa da Yahaya Hasanu, Zahara Mu’azu da Ibrahim Dayyabu. Haka kuma maharan sun yi garkuwa da mutum shida daga cikin mazauna ƙauyen.
An ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe ɗaya na dare a ranar Talata, inda maharan suka shafe kusan sa’o’i biyu suna harbe-harbe tare da sace dabbobi.
Wani mazaunin ƙauyen ya ce, “Muna salla da dare lokacin da muka fara jin harbi daga ko’ina. Mun tayar da iyalanmu daga bacci muka gudu bayan ƙauye domin tsira da rayukanmu.”
Rahotanni sun kuma nuna cewa maharan sun shiga gida-gida suna sace mutane, musamman matan aure, yayin da suka kashe wasu da suka ƙi bin su zuwa daji.
Ƴanbîndïga Sun HaIIaka Limami Da Wasu Mutum 3 a Sokoto

